Ma'aikatar kula da harkokin farfaganda na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da hukumar kula da harkokin radio da telebijin ta kasar da kuma ma'aikatar kula da harkokin jama'a ta kasar sun wallafa wannan taro, inda aka bayar da wasu labarai game da aikin ceto da aka gudanar a mako daya bayan abkuwar girgizar kasa a yankin Yushu, da yin wasanni da aikin bayar da kudin taimako don jajantawa jama'a masu fama da bala'in a madadin dukkan jama'ar kasar Sin. Ban da wannan, an bayar da kudin taimako kai tsaye a gun taron, kana masu kallon taron ta kwatunan telebijin sun bayar da kudin taimako ta hanyar buga waya.(Zainab)