in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasa da kasa sun nuna yabo ga aikin ceto da ake gudanarwa a yankin Yushu
2010-04-20 14:28:58 cri

Bayan abkuwar girgizar kasa a yankin Yushu dake lardin Qinghai na kasar Sin, kasa da kasa sun nuna yabo ga aikin ceto da ake gudanarwa bisa jagorancin gwamnatin kasar Sin, kana suna fatan jama'a masu fama da bala'in za su warware matsaloli da aka fuskanta da sake gina gidajensu.

Firaministan kasar Tanzania Mizengo Kayanza Peter Pinda ya jajantawa gwamnatin kasar Sin da jama'arta bayan abkuwar girgizar kasar, kana yana nuna yabo ga kasar Sin da ta dauki matakan ceto ba tare da bata lokaci ba. Ya kuma nuna yabo ga shugaban kasar Sin Hu Jintao da firaminstan kasar Wen Jiabao da suka isa yanki mai fama da bala'in, da ba da jagoranci ga aikin ceto, da zama tare da jama'a masu fama da bala'in a lokacin.

Ministan harkokin waje na kasar New Zealand Murray McCully ya bayar da wata sanarwa, inda ya ce, kasar Sin tana da wani tsari mai inganci na tinkarar bala'u cikin gaggawa. A matsayin wata muhimmiyar abokiyar kasar Sin, kasarsa za ta ba da taimakon kudi da ya kai kimanin dala dubu 280 ga yankin Yushu.

Jaridar Wall Street Journal ta kasar Amurka ta bayar da wani labari, inda ta ce, an fara yin jigilar kayayyakin taimako zuwa yankin Yushu. Kazalika shugaba Hu Jintao ya kammala ziyararsa da wuri a nahiyar Latin Amurka, kuma ya isa yankin Yushu a ran 18 ga wata don ba da jagoranci ga aikin ceto. Shugabannin kasar Sin sun taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da aikin ceto. Jama'ar dake zauna a yankin sun bayyana cewa, ziyarar da Hu Jintao da Wen Jiabao suka kai a yankin, tasa mutane sun kwantar da hankali.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China