Rahoto daga kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya ce, majalisar gudanarwa ta kasar Sin ta yanke shawarar cewa, domin nuna babban alhini ga mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon bala'in girgizar kasa da ya abku a gundumar Yushu dake lardin Qinghai na kasar Sin, za'a yi zaman makoki a ranar 21 ga watan Afrilu na shekara ta 2010, inda za'a sassauto da tutocin kasar a dukkan kasar Sin da ofisoshin jakadancin kasar dake ketare, gami da dakatar da dukkanin shagulgula.(Murtala)