in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hu Jintao ya je gundumar Yushu da ta yi fama da girgizar kasa don yin jagorancin aikin ceto
2010-04-19 18:06:14 cri

A ranar 18 ga wata da safe, Hu Jintao, shugaban kasar Sin ya iso gundumar Yushu ta lardin Qinghai da ke yammacin kasar Sin, inda aka samu bala'in girgizar kasa mai tsanani, don ya nuna juyayi ga jama'ar wurin, sa'an nan ya yi jagorancin aikin zakulo mutane daga baraguzan gine-gine.

Lokacin da aka samu rahoton aukuwar girgizar kasa mai karfin maki 7.1 bisa ma'aunin Richter a ranar 14 ga wata a gundumar Yushu ta lardin Qinghai, Shugaba Hu Jintao yana birnin Washington na kasar Amurka inda ya halarci shawarwarin da aka yi don neman hana yaduwar makaman nukiliya, daga bisani ya kai ziyara a kasar Brazil. Bayan haka kuma, shugaban ya koma kasar Sin a ranar 17 da yamma kafin lokacin da aka tsara. Nan da nan, Hu ya wuce gundumar Yushu a ranar 18 da safe, da kuma yin rangadi a kauyen Zhaxidatong inda aka tabka mummunar hasara sakamakon girgizar kasa. A gaban baraguzan gidaje, Hu ya rike hannun wani mazaunin wurin yana cewa, 'Za mu yi kokarin ceto wadanda suke karkashin baraguzan gidaje. Duk da cewa muna samun mutanen da ke da sauran numfashi a karkashin kasa, to, za mu yi bakin kokarin kubutar da su!'

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China