in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
lardin Gansu ya zuba kudin Sin yuan biliyan 20 domin kyautata ingancin gidajen kwana na jama'a
2010-04-19 10:59:09 cri

A kwanan baya, gwamnatin lardin Gansu da ke yammacin kasar Sin ta sanar da cewa, za ta kebe kudin Sin fiye da yuan biliyan 20 a bana domin kyautata gidajen kwana na jama'ar lardin.

An labarta cewa, daga cikin wadannan kudade yuan biliyan 20, za a kebe kudin Sin yuan miliyan dari 8 domin kyautata ingancin gidajen kwana da yawansu zai kai dubu dari 2 a yankunan karkara, sannan za a kebe kudin Sin yuan biliyan 12 da miliyan dari 6 domin kyautata gidajen kwana da yawansu zai kai dubu 63.7 a birane, har ma za ta kebe kudin Sin yuan biliyan 1 da miliyan dari 5 domin gina gidaje masu rahusa da yawansu zai kai murabba'in mita miliyan 1 a birane. Bugu da kari, za a kebe kudin Sin yuan biliyan 5 da miliyan dari 7 domin sake gina gidajen kwana ga wadanda suke zaune a yankunan da suka gamu da bala'in girgizar kasa mai tsanani sosai a shekarar 2008.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China