Yawan mutanen da suka mutu a sanadiyyar abkuwar girgizar kasa a gundumar Yushu ta kasar Sin ya karu zuwa 1339
A gun taron manema labarai da aka shirya a ranar 17 ga wata da yamma, kakakin ofishin ba da jagoranci kan harkokin samar da agaji ga yankin da ke fama da girgizar kasa a lardin Qinghai da ke arewa maso yammacin kasar Sin, Xia Xueping ya bayyana cewa, ya zuwa wannan rana da safe, da misalin karfe 10, yawan mutanen da suka rasa rayukansu a sakamakon girgizar kasar da ya abku a gundumar Yushu ta lardin Qinghai ya kai 1339, a yayin da wasu 332 suka bace. Sa'an nan, 11,849 suka ji raunuka.(Lubabatu)