in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jia Qinglin ya yi jawabi a gun taron tattaunawa da wakilan masana'antun Sin da ke kasar Afrika ta kudu
2010-03-31 20:34:13 cri

A ranar 31 ga watan Maris, a birnin Pretoria, shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin Jia Qinglin ya yi jawabi a gun taron tattaunawa da wakilan masana'antun kasar Sin da ke kasar Afrika ta kudu.

Jia Qinglin ya gabatar da kyawawan fata gare su, ya ce, na farko ta fanning yin kokari wajen samun bunkasuwa a kasuwannin kasashen Afrika. Sai, yin hobbasa don taimakawa kasashen Afrika wajen kyautata zaman rayuwar al'umma a wurin, domin kiyaye kwarjinin masana'antunsu da na kasar Sin. Kana da batun kafa tsarin hadin gwiwa a fannin tattalin arziki da cinikayya da kasashen Afrika, domin daidaita lamura tare.

Wakilan masana'antun da ke halartar taron, sun bayyana cewa, masana'antun Sin a kasar Afrika ta kudu za su ci gaba da kiyaye manufar samun moriyar juna cikin jituwa tare, da yin kokari wajen raya sana'o'insu da gudanar da hakikanin ayyuka a wurin, domin kokarin fadada hadin gwiwa kan sha'anin tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika, da kara yin kokari wajen sa kaimi ga sha'anin raya tattalin arzikin kasar Sin da sada zumunci tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China