in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana fatan samar da tallafi ga kasashen da za su halarci taron baje-koli na Shanghai cikinsu har da Koriya ta arewa
2010-03-30 20:19:39 cri

A ranar 3 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya bayyana a nan birnin Beijing cewa, taron baje-koli na Shanghai zai zama gagarumin biki da za a inganta mu'amala da hadin gwiwa da kara fahimtar juna tsakanin kasashen duniya, sabo da haka, kasar Sin tana maraba da kasashen duniya, cikinsu har da Koriya ta arewa, don halartar taron, kuma tana fata za ta sa himma wajen samar da tallafi da sauki gare su.

Qin Gang ya fadi haka ne a yayin taron manema labaru da ma'aikatar harkokin wajen Sin ta shirya a wannan rana.

Taron baje-koli na Shanghai zai zama taron baje-koli na farko da kasar Koriyar ta arewa za ta halarta. Bisa labarin da aka samu, an ce, yanzu, kasar Koriya ta arewa ta riga ta share fagen halartar taron, kuma an kusan kawo karshen aikin giggina dakuna da filaye na kasar Koriya ta arewa. Nan ba da dadewa ba, za a gudanar da aikin gwaji. Babban taken kasar Koriya ta arewa a gun taron baje-koli na Shanghai, shi ne "Raya birnin Pyangyong mai wadata, bisa al'adu na kogin Taedong-Gang".(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China