in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jia Qinglin ya isa birnin Cape Town don fara ziyarar aiki a kasar Afirka ta Kudu
2010-03-28 20:06:43 cri

A ran 28 ga wata da yamma, Jia Qinglin, shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin ya isa birnin Cape Town, babban birnin kasar Afirka ta Kudu ta fuskar kafa doka don fara ziyarar aiki a kasar Afirka ta Kudu bisa gayyatar da kwamitin kula da harkokin jihohi na kasar ya yi masa.

Jia Qinglin ya yi jawabi a filin jiragen sama, inda ya fadi cewa, tun bayan da aka kulla huldar diplomasiyya a tsakanin kasashen Sin da Afirka ta Kudu a shekara ta 1998, ana raya dangantakar da ke tsakaninsu cikin sauri. Bangarorin biyu sun tabbatar da kulla dangantakar abokantaka don zaman daidai wa daidai da moriyar juna kana da samun bunkasuwa tare bisa manyan tsare-tsare, kuma suna karfafa amincewar juna ta fuskar siyasa. Haka kuma sun samu sakamako mai kyau wajen hadin kansu a fannonin tattalin arziki da cinikayya da al'adu da ilmi da kimiyya da fasaha kana da yawon shakatawa, kuma suna ta inganta hadin gwiwarsu a cikin al'amuran duniya da na shiyya-shiyya.

Haka kuma Jia Qinglin ya furta cewa, kasashen Sin da Afirka ta Kudu muhimman kasashe masu tasowa ne. Don haka ba kawai inganta dangantakarsu na dacewa da babbar moriyar kasashen biyu da jama'ar kasashen biyu ba, har ma zai ba da taimako wajen sa kaimi ga samun zaman lafiya da bunkasuwar duniya gaba daya.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China