in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta nace ga samun bunkasuwa cikin lumana da kuma inganta hadin gwiwa da kasa da kasa cikin yakini
2010-03-14 20:45:47 cri

Firayim ministan kasar Sin Wen Jiabao ya bayyana a ran 14 ga wata a birnin Beijing, cewar bunkasuwar kasar Sin ba za ta yi illa ga ko wace kasa ba. Kasar Sin ba ta nuna isa ba yayin da take baya baya, ko da kasar Sin ta samu babban ci gaba a nan gaba, to ba za ta nuna isa a duniya ba har abada. A waje daya kuma, kasar Sin za ta ci gaba da inganta hadin kai tare da kasashen duniya cikin yakini.

Wen Jiabao ya furta cewa, ko da yake kasar Sin ta samu saurin bunkasuwar tattalin arziki a 'yan shekarun da suka gabata, amma sakamakon rashin samun daidaito a tsakanin birane da yankunan karkara, da kuma tsakanin wurare daban daban, kana da samun yawan mutane da tushen tattalin arziki maras inganci, za a kwashe shekaru 100 ko fiye in kasar Sin tana son kaiwa matsayin zamanintarwa.

Haka kuma Mr. Wen ya jaddada cewa, Sin ta nace ga bin hanyar samun bunkasuwa cikin lumana. A matsayinta ta wata kasa da ke daukar alhaki a kai, Sin tana tsayawa kan ra'ayin inganta hadin kai tare da kasa da kasa cikin yakini domin warware manyan batutuwan da ke gaban duniya a fannonin tattalin arziki da siyasa. Sin tana samar da taimako ga kasashe masu fama da talauci ne ba tare da ko wane sharadi ba.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China