in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta ci gaba da yin kokari tare da kasa da kasa domin tinkarar sauyawar yanayi
2010-03-14 17:45:52 cri

Firayim ministan kasar Sin Wen Jiabao ya yi bayani a ran 14 ga wata a birnin Beijing, cewar kasar Sin tana nuna babban yabo da kuma goyon baya ga kudurin taron Copenhagen, kuma za ta ci gaba da yin kokari tare da kasashe daban daban domin tinkarar sauyawar yanayi.

Wen Jiabao ya gana da manema labarun gida da na waje bayan da aka rufe taron shekara shekara na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, inda ya furta cewa, batun sauyawar yanayi yana da nasaba da kasancewar bil Adam a duniya, da muradun kasashe daban daban, kana da samun daidai wa daida da adalci a duniya. Ka'idar "daukar nauyi tare amma akwai bambanci" da kasar Sin ke tsayawa tsayin daka a kai ta yi daidai sosai, kasar Sin kuma za ta ci gaba da hadin kai tare da kasashen duniya domin sa kaimi ga yunkurin tinkarar sauyawar yanayi.

Ban da wannan kuma, Wen Jiabao ya bayyana cewa, kasar Sin za ta samar da wani kyakkyawan muhalli ga kamfanonin waje bisa doka ta yadda za su iya raya ayyukansu cikin daidai wa daida, da kuma more gata ta musamman kamar yadda kamfanonin kasar Sin ke yi. (Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China