in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mugun nufi ne ya sa aka zargi kasar Sin da boye kudin ayyukan soja
2010-03-11 19:26:03 cri

Bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na Xinhua na kasar Sin ya bayar a ran 11 ga wata, an ce, a lokacin da yake zantawa da manema labaru, Jia Yong, mamban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin ya bayyana cewa, dalilin da ya sa wasu kafofin yada labaru na kasashen yammacin duniya suka zargi kasar Sin da boye kudin aikin soja shi ne mugun nufi da suke da shi.

Jia Yong, shugaba ne na sashen harkokin soja na kamfanin dillancin labaru na Xinhua. Ya yi nuni da cewa, a shekaru 10 ko fiye da suka wuce, a ko wadanne shekaru 2 kasar Sin ta kan kaddamar da takarda kan harkokin tsaron kasa, inda take yin karin bayani kan harkokin tsaron kasa da yadda ake bunkasa soji filla-filla, haka kuma bayanin da ta kan yi kan kudin aikin soja ya fi na dimbin kasashen duniya yawa.

Mr. Jia Yong ya kuma ci gaba da cewa, bisa kasafin kudi da kasar Sin ta kebe a aikin soja a shekarar 2010, an ce, matsakaicin kudin da ko wane mutumin Sin zai kashe a aikin soja ya kai kashi daya daga cikin kashi gomai bisa na ko wane mutumin kasar Amurka. Sa'an nan, yawan kudin da kasar Sin ta kashe a aikin soja ya kai kashi 1.4 cikin dari bisa jimillar GDP da ta samu. A yayin da matsakaicin adadi a wannan fanni a duniya ya kai kashi 2.5 zuwa 3 cikin dari.

Mr. Jia Yong ya nuna cewa, bisa ga hakikanin gaskiyar abin sannu a hankali, zargin da ake yi wa kasar Sin na cewa, za ta kawo barazana zai ci tura. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China