in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kafofin watsa labaru na kasashen waje sun mai da hankali kan rahoton gwamnatin kasar Sin dangane da aikinta
2010-03-05 20:40:32 cri

An bude taro a karo na 3 na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ta 11 a ranar 5 ga wata, inda Wen Jiabao, firayin ministan kasar Sin, ya ba da rahoto kan aikin gwamnatin kasar. Sa'an nan, kafofin watsa labaru na kasashen waje sun fitar da labarai da yawa kan manufofin tattalin arziki na kasar Sin da aka ambata a cikin rahoton da Mista Wen ya bayar, inda musamman ma aka mai da hankali kan matakan kudi masu yakini da sassauci da kasar Sin ta ci gaba da tsayawa a kai, da kuma manufarta ta kiyaye zaman karko na darajar musayar kudin kasar.

Kamfanin dillancin labaru na The Associated Press na kasar Amurka ya ambato Mista Wen Jiabao yana cewa, kasar Sin za ta yi kokarin cimma burinta na samun karuwar yawan kudin kayayyakin da ake samarwa gida da kashi 8% a bana. Haka zalika kuma, rahoton Mista Wen ya bayyana cewa, kasar za ta tabbatar da farfadowar tattalin arzikinta wanda ya zama na 3 a duniya, ta hanyar hana hauhawar farashin kaya da sa ido kan tsarin hada-hadar kudi.

Ban da haka kuma, kamfanin Reuters na kasar Birtaniyya ya ba da labarin cewa, rahoton aikin gwamnatin kasar Sin da Mista Wen Jiabao ya bayar ya sa ana hangen karuwar tattalin arzikin kasar cikin sauri inda ake sa ran ci gaba da samu a nan gaba, sa'an nan, ana kyautata zaton cewa, gwamnatin kasar Sin za ta kara kokari wajen shawo kan hauhawar farashin kaya da aikin ba da lamuni don magance yiwuwar rashin alfanu a fannin tattalin arziki.

A baya ga haka kuma, jaridar Wall Street Journal ta kasar Amurka ta ba da labarin cewa, kasar Sin ta zama mai tattalin arzikin da ya fi saurin bunkasuwa a duniya, sa'an nan, jawabin Mista Wen Jiabao zai bayyana fuskar da tattalin arzikin zai nufa a nan gaba.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China