A ran 3 ga wata da yamma, a birnin Beijing, an bude taro na uku na majalisar ba da shawarwari kan harkokin siyasa na 11 na jama'ar kasar Sin. Hu Jintao da Wu Bangguo da Wen Jiabao da Jia Qinglin da sauran shugabannin kasar Sin sun halarci bikin budewar taron.
Taron majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama'ar kasar Sin wata muhimmiyar hukuma ce ta hadin gwiwar jam'iyyu da dama da ba da shawarwari kan harkokin siyasa da ke karkashin jagorancin jam'iyyar kwaminis ta Sin. A cikin kwamaki 10 masu zuwa na taron, membobi fiye da 2100 na majalisar da suka fito daga jam'iyyu daban daban da kabulu sassa daban daban za su tattaunawa da ba da shawarwari kan batutuwan da ke da nasaba da siyasa da tattalin arizki da kuma zaman al'ummar kasar.(Abubakar)