in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An shiga matakin karshe na share fagen bude kofar dakin nune-nune na hadin gwiwar Afirka a EXPO
2010-01-23 20:22:11 cri

Ran 23 ga wata, a dandalin taron baje-koli na duniya a birnin Shanghai na kasar Sin, an shirya harkokin karfafa gwiwa a dakin nune-nune na hadin gwiwar Afirka saboda an shiga matakin karshe na share fagen bude kofar wannan dakin nune-nune.

A cikin wadannan harkoki, shugabannin kungiyoyi kusan 20 na ba da hidima a cikin dakin nune-nune na hadin gwiwar Afirka sun nuna fatansu na gudanar da harkokin nune-nune bisa ajandar ayyuka, ta haka za a iya samar da dakin nune-nune mai kayatarwa.

A yayin taron baje-koli na duniya da za a yi a birnin Shanghai na kasar Sin, kungiyar tarayyar Afirka da kasashe 42 na Afirka za su kasance cikin dakin nune-nune na hadin gwiwar Afirka. Yawansu ya fi yawa a tarihin dakin nune-nune na hadin gwiwar Afirka a yayin taron baje-koli na duniya.

Haka kuma, dakin nune-nune na hadin gwiwar Afirka dakin nune-nune ne mafi girma a cikin dukkan dakunan nune-nune na hadin gwiwa a dandalin taron baje-koli na duniya na Shanghai. Yanzu ana yi masa ado da kuma gudanar da harkokin nune-nune cikin himma da kwazo.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China