in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jaridar Al-Sabah ta kasar Morocco ta ruwaito bayanin da ministan harkokin waje na kasar Sin Yang Jiechi ya bayar
2010-01-11 09:19:52 cri
A kwanan baya, jarida mafi girma na kasar Morocco wato Al-Sabah ta ruwaito bayani mai suna "bunkasuwar zumanci na gargajiya tare da dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka" da ministan harkokin waje na kasar Sin Yang Jiechi ya bayar.

A cikin bayanin, an ce, dangantakar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka nada karfi sosai. Dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka wanda ci gaba da kara amincewa da juna a fannin siyasa da yin hadin gwiwa a fannin tattalin arziki da koyi da juna a fannin al'adu ya dace da moriyar Sin da kasashen Afirka.

Tun daga ran 5 zuwa 14 ga wata, Yang Jiechi yana yin ziyara a kasashe 5 na Afirka da kasar Saudiyya da kasar Maldives. A cikin bayanin, ya jaddada cewa, yin hadin gwiwa tare da kasashe masu tasowa da ke hade da kasashen Afirka shi ne manufofin kasar dangane da harkokin waje.

A cikin bayanin, an ce, a cikin 'yan shekaru da suka wuce, dangantakar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka ta samu bunkasuwa sosai, musamman ma a cikin yanayin matsalar kudi ta duniya, hadin gwiwa da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka ya zaman muhimmin aiki na duniya.(Abubakar)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China