in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan GDP na kasar Nijeriya a shekarar 2009 ya karu da kashi 6.9%
2010-01-07 09:27:36 cri

A ran 5 ga wata, bankin tsakiya ta kasar Nijeriya ta ce, yawan GDP da kasar ta samu a shekarar 2009 ya karu da kashi 6.9%, wanda ya karu da 1% bisa na shekarar 2008, kana ya karu bisa zaton da bankin duniya ta yi kan karuwar tattalin arzikin yankin kudancin Sahara wato kasa da kashi 5%.

Shugaban bankin tsakiya na kasar Nijeriya Lamido Sanusi ya bayyana cewa, muhimmin dalilin da ya sa tattalin arzikin kasar ya samu bunkasuwa ba domin sana'ar man fetur kawai ba, saidai a ce aikin noma da sana'ar yawon shakatawa da sana'ar sadarwa suka taimaka kwarai wajen wannan bunkasa. Karuwar sana'ar kere-kere ba ta kai kashi 1% a cikin karuwar GDP ba, amma karuwar aikin noma ta kai fiye da 40% a cikin karuwar GDP.

Mr Sanusi ya ce, karuwar tattalin arziki ba ta samar da karin damar samun aikin yi ba, domin sana'ar kere-kere da ta fi samar da aikin yi tana fuskantar matsalolin ayyukan yau da kullum marasa ci gaba da rashin tallafin bayar rancen kudi.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China