in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An samu sakamako mai kyau a yayin taro na 17 tsakanin shugabannin kasashe membobin kungiyar APEC
2009-11-15 15:43:14 cri

Ranar 14 ga wata da yamma, a yayin taron manema labarai na gida da waje da aka shirya a cibiyar watsa labarai ta tawagar kasar Sin dake kasar Singapore, shugaban sashin kula da harkokin waje na ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Mista Wu Hailong ya bayyana yadda aka gudanar da zaman taro a mataki na 1 na kwarya-kwaryan taro a karo na 17 tsakanin shugabannin kasashe membobin kungiyar APEC.

Mista Wu ya ce, babban taken taron da aka yi a ranar 14 ga wata da maraice shi ne "inganta mu'amala a wannan yanki", inda aka yi tattaunawa mai zurfi kan 'yantar da harkokin ciniki a yankunan Asiya da Pacific, da bude kasuwanni da sauransu, haka kuma an cimma sakamako mai kyau tsakanin bangarori daban-daban.

A waje guda kuma, shugabanni mahalarta taron sun cimma matsaya kan nuna adawa ga kowane irin ra'ayin bada kariya ga harkokin ciniki, haka kuma sun sake jaddada alkawarin da suka dauka na cewa, ba za su kafa sabon shinge ba ga harkokin ciniki da zuba jari, kuma za su duba wannan batu lokaci-lokaci.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China