Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-09-22 15:45:10    
Thabo Mbeki ya yi murabus daga mukamin shugaban kasar Afirka ta kudu

cri

A ran 21 ga wata, Mr. Thabo Mbeki, shugaban kasar Afirka ta kudu ya bayar da wani jawabi a gidan talibijin kasar, inda ya sanar da yin murabus daga mukaminsa na shugaban kasar Afirka ta kudu. A cikin jawabinsa, Mr. Mbeki ya ce, shi da gwamnatinsa ba su taba tsoma baki kan harkokin shari'a ba, kuma ba su taba sa hannu kan hukumar bincike ta kasar da ta kai kara ga Jacob Zuma, shugaban yanzu na jam'iyyar Taron Jama'ar Afirka ta kudu, wato ANC da laifin rashawa da al'amubazzaranci. Amma domin tabbatar da hadin kai a cikin jam'iyyar. Ya yanke hukuncin amincewa da kudurin neman shi da ya yi murabus daga mukaminsa na yanzu da jam'iyyar ANC ta yi, kuma ya riga ya gabatar da wasikar neman yin murabus daga mukaminsa ga majalisar dokokin kasar Afirka ta kudu. Wannan ya almanta cewa, za a kawo karshen lokacin Thabo Mbeki a dakalin siyasa na kasar Afirka ta kudu, kuma za a samu wani sabon shugaba a kasar.


1 2 3 4