Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'a ya zartas da shawara game da Hong Kong
2020-11-11 19:32:10        cri
A yau ne, aka kammala zaman taro karo na 23 na zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'a na 13 a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. Taron ya kuma kada kuri'a tare da amincewa da "shawarar da zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'a ya yanke game da soke wasu mambobin majalisar dokokin yankin musamman na Hong Kong na kasar Sin."

Shawarar ta bayyana karara cewa, mambobin majalisar dokokin yankin musamman na Hong Kong, sun yayata ko goyi bayan neman 'yancin kan Hong kong", ko neman kasashen ketare ko wasu daga ketare su tsoma baki a harkokin yankin musamman na Hong Kong, ko aikata wasu ayyuka dake da hadari ga tsaron kasar. Idan har suka gaza cimma ka'idoji ko sharudda na martaba muhimman dokokin yankin musamman na Hong Kong na jamhuriyar jama'ar kasar Sin da martaba yankin musamman na Hong Kong na jamhuriyar jama'ar kasar Sin, aka kuma tabbatar bisa doka, to za a iya soke matsayinsu na zama mamba a majalisar dokoki ba tare da bata lokaci ba. (Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China