Xi Jinping ya kai ziyarar aiki a lardin Anhui
Yau Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyarar aiki a lardin Anhui na kasar Sin. Kana da yamma, ya ziyarci madatsar ruwa ta Wangjiaba dake garin Funan na birnin Fuyang, domin ganewa idonsa yanayin da kogin Huai ke ciki. Daga bisani kuma, ya ziyarci wasu gonaki, domin ganin yadda aka farfado da ayyukan gona bayan ambaliyar ruwa, ya kuma gaisa da al'ummomin da bala'in ya shafa. (Maryam)
Labarai masu Nasaba