![]() |
|
2020-04-30 11:41:10 cri |
Le Yucheng ya bayyana haka ne yayin zantawa da kafar yada labarai ta Amurka a ranar Talata.
Ya ce kasar Sin na gudanar da harkokinta a bayyane kuma bisa gaskiya, kuma tana goyon bayan masayar bayanai tsakanin kwararrun kimiyya, ciki har da musayar nazarin yanayin da ake fuskanta.
Amma a cewarsa, abun da take adawa da shi, shi ne, tuhuma ba tare da hujja ba, yana mai cewa, bai kamata a fara da zargin kasar ba, sannan kuma a gudanar da bincike kawai saboda a kirkiro hujja. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China