Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Ma'aikatar wajen Sin ta yi watsi da zargin cewa wai COVID-19 ta samo asali ne daga dakin gwaji a Wuhan
2020-04-20 20:48:50        cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng shuang, ya yi watsi da jita-jitar da wasu jami'an kasar Amurka ke yadawa, cewa wai cutar numfashi ta COVID-19 ta samo asali ne daga wani dakin gwaji, na cibiyar binciken kimiyya dake birnin Wuhan.

Geng shuang wanda ya yi tsokaci kan wannan batu a Litinin din nan, ya sake jaddada cewa, batun cutar COVID-19, batu ne na kimiyya, wanda sam bai dace a siyasantar da shi ba. Ya ce ba wata shaida dake tabbatar da wancan zargi na jami'an Amurka. Don haka kasar Sin ke fatan irin wadancan mutane za su rika mutunta gaskiya, da kimiyya da ra'ayin al'ummun kasa da kasa.

Geng ya kara da cewa, cibiyar gwaje gwajen kimiyya ta Wuhan na da managarcin tsarin gudanarwa, kuma ba wani jami'in ta ko da guda daya da ya kamu da cutar COVID-19. Kaza lika jami'an cibiyar na aiki tukuru wajen aiwatar da bincike na kimiyya.

Ya ce furta zargi maras tushe da labaran kanzon kurege da wasu jami'an Amurka ke yi, ba zai haifar da komai ba sai illata binciken kimiyya, da gurgunta hadin gwiwar dake tsakanin masana kimiyyar Sin da na Amurka. (Saminu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China