![]() |
|
2020-04-19 21:40:28 cri |
A halin yanzu, kananan ofisoshin jakadancin kasashen Afrika dake Guangzhou sun bullo da wasu shirye shiryen tuntubar juna tsakaninsu da gwamnatin lardin Guangdong da ta birnin Guangzhou, domin a samu hakikanin fahimta game da matakan yaki da annobar COVID-19 ta Guangdong da kuma tsare tsaren da suka shafi hadin gwiwa domin yaki da annobar, a cewar Alima Danfakha Gakou, shugabar wakilan kasashen Afrika dake Guangzhou, kana jami'ar dake kula da karamin ofishin jakadancin kasar Mali a birnin Guangzhou, ta bayyana cewa, aminantaka da hadin gwiwa dake tsakanin Sin da Afrika dawwamamme ne. Ta kuma nuna fatan dukkan bangarorin za su yi aiki tare domin dakile barazanar annobar, da kuma kiyaye lafiyar al'umma.(Ahmad Fagam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China