Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
'Yan bindiga sun hallaka mutane 4 a wani kauye dake jihar Plateau
2019-06-19 20:15:48        cri
Rahotanni daga jihar Plateau dake tsakiyar tarayyar Najeriya, na cewa wasu 'yan bindiga sun hallaka mutane hudu ciki hadda soja daya, lokacin da suka kai farmaki kauyen Rong mai makwaftaka da Ganawuri a karamar hukumar Riyom dake jihar.

Da yake karin haske game da harin, dan majalissar dokokin jihar Timothy Datong, ya ce yayin harin na yammacin ranar Litinin, 'yan bindigar sun kone a kalla gidajen kwana 54, kana sun lalata gonaki da dama, lamarin da ya tilasawa mazauna kauyen barin muhallansu.

Mr. Datong ya ce yanayin tsaro a jihar musamman a wannan lokaci na zama mai matukar ban tsoro.

Kawo yanzu dai rundunar 'yan sandan jihar ta ce ba bu cikakken bayani, game ko su waye suka kaddamar da harin, da ma dalilin aukuwar sa. (Saminu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China