Yadda za a kara hada kai ta fuskar al’adu tsakanin kasashen biyu

Mu’amala ta cinikayya tsakanin Nijeriya da China

Wannan abu wanda ke da karfi, a halin yanzu, mu Nijeriya muke da bukatar kasar Sin shigo mana ta sigar, yadda za su taimakawa masana’antunmu da al’ummarmu, ba wai su zo ne, don su yi ciniki, su sami abin duniya, su tafi, a’a sun dauko dukiyarsu, su kawo Nijeriya su sami harkar hadin gwiwa tsakaninsu da mutanen Nijeriya, mu ma mun amfana, su ma sun amfana, jama’armu sun sami aiki, kuma an sami ci gaba gaba daya.

Ra’ayin Alhajji kan Taron baje-koli na Shanghai

Wannan ina kira wa dukkan ‘yan kasuwanni namu manya-manya da kuma kamfanoni manya-manya na Nijeriya da suka zo wannan kasar China, don halartar taron baje-koli na Shanghai, don za su iya ganin irin abubuwan da suke faruwa a kasar Sin, da kuma kamfanonin da za su iya hulda da su, da wadanda za su zuwa Nijeriya, su je su kafa masana’antu, ko dai da kansu ko kuma hadin gwiwa da Nijeriya, to, wannan kasuwa ce za ta ba da dama, dukkanin ‘yan kasuwa na kirki, ya zo ya gani halin wannan taron baje-koli, wanda za a gani, zai ba da dama.

Nijeriya za ta nuna abubuwan da take da shi, na dukiyoyin kasarta, wanda China take bukatarta, kamar kayan amfanin gona, da ma’adinai, da mai da dai dukkan abubuwan da za a iya samun riba ta hulda kansu da China, mun ma, za mu nuna taimako da gwamnati take bayarwa, ga dukkanin mutanen da suke da sha’awa, su zo, su yi harkar cinikayya, gwamntin Nijeriya za ta taimake gare su, kuma mu taimako wajen hutun haraji.