Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Minista: Akwai yuwuwar sinadarai masu fashewa ne suka haifar da gobarar tashar ruwan Beirut
2020-08-05 10:35:12        cri
Ministan harkokin cikin gidan Lebanon, Mohammad Fahmi, ya ce akwai yuwuwar sinadarai masu fashewa da aka adana a tashar ruwan Beirut ne suka haddasa fashewar da ta haddasa asara da jikkatar mutane.

Gidan talabijin na al-Jadeed, ya ruwaito ministan na cewa, akwai yuwuwar sinadarin Ammonium nitrate da aka ajiye a wani dakin adana kayayyaki mai lamba 12 a tashar ruwan tun shekarar 2014 ne ya haifar da gobarar.

Ya ce za a tuhumi hukumomin kwastam game da dalilan da suka sanya aka adana sinadarai a tashar ruwan ta Beirut.

Ministan ya kuma tabbatar da cewa an shawo kan kaso 80 na gobarar da fashewar ta haifar.

Shugaban Lebanon Michel Aoun, ya kira wani taron gaggawa na majalisar tsaro domin tattauna musabbabi da abun da ya biyo bayan gobarar. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China