2020-03-16 19:42:32 cri |
Tawagar da kasar Sin ta tura ta kunshi kwararrun aikin kiwon lafiya 9, wadanda suka tashi daga birnin Shanghai na kasar Sin, sa'an nan suka isa birnin Rome na kasar Italiya a ranar Alhamis da ta gabata, tare da dimbin kayayyaki da na'urorin da ake bukata. Daga bisani gwamnatin kasar Italiya ta kira taron manema labaru a ranar Jumma'a, musamman ma domin maraba da tawagar kwararrun kasar ta Sin. (Bello Wang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China