Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sojin gwamnatin Somaliya sun harbe mambobin kungiyar Al-Shabaab 8
2019-12-24 13:27:55        cri

Jiya Litinin, sojin gwamnatin Somaliya sun yi musanyar wuta da masu tada kayar baya na kungiyar Al-shabaab a kudancin kasar, inda suka harbe mayakan kungiyar 8 har lahira. A nata bangaren kuwa, kungiyar ta ce, ta kashe sojojin gwamnati kasar su 8.

Kungiyar Al-shabaab na da alaka sosai da kungiyar Al-Qaeda, wadda ta dade take aiwatar da ayyukan ta'addanci a Somaliya, da masu wasu kasashe masu makwabtaka. (Amina Xu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China