Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Wang Yi: Dole a rungumi akidun daidaito da adalci da cin moriyar juna idan ana son cimma nasarar cudanya da juna
2019-12-16 21:32:23        cri
A yau Litinin ne dan majalissar gudanarwa, kuma ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, ya bayyana cewa, dole sai an rungumi manufofin daidaito da adalci, da cin moriyar juna, idan har ana da burin cimma nasarar cudanya tsakanin sassan duniya.

Wang Yi ya bayyana hakan ne, a yayin taron ministocin waje na 14 na kungiyar ASEM, wanda ya gudana a birnin Madrid na Sifaniya. Yana mai cewa manufar cudanyar sassa daban daban, ba za ta yi nasara ba, har sai an wanzar da zaman lafiya, an kuma bunkasa ci gaba. Ya ce cudanyar sassa daban daban shi ne jigon warware kalubalen dake addabar duniya.

Ministan ya kara da cewa, ko wane irin tsari za a bi na cudanyar sassa daban daban, burin sa shi ne wanzar da zaman lafiya a duniya, da kuma samun ci gaba. Ya ce ya dace kasashen Asiya da na turai, su samar da wani misali a fannin kare cudayyar sassa daban daban, su nacewa manufar gudanar da al'amura a mataki na kasa da kasa da hadin gwiwar MDD a matsayin ginshiki, su kuma wanzar da tsarin ciniki da zai hade sassa mabanbanta, karkashin kungiyar cinikayya ta duniya WTO a martsayin ginshiki. (Saminu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China