2019-09-28 20:44:41 cri |
Amma mai nema yana tare da samu. Bayan da kasar Sin ta gabatar da dokar ba da ilimin tilas a shekarar 1986, sannu a hankali ta tabbatar da wannan tsari na ba da ilimin tilas kyauta ga dalibai wadanda shekarunsu ke tsakanin 6 zuwa 15, a dukkan sassan kasar, bayan shekaru 20 da ta dauka tana kokarin raya wannan tsari. A sa'i daya kuma, an yi kokarin raya harkokin jami'o'i da makarantun koyar da ilimin sana'a a kasar, har ma an samu karin mutanen da suka yi karatun jami'a da suka kai miliyan 270 cikin shekaru 70 da suka wuce.
Bisa manufar kasar Sin, za a kara mai da hankali kan raya masana'antu masu inganci, wadanda ke samar da kayayyaki masu daraja a kasar, inda masu ilimi za su kara taka rawar gani a kokarin taimakawa kasar cimma burinta.(Bello Wang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China