Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sojojin Niger da Faransa sun harbe 'yan ta'adda 18
2019-06-21 10:25:35        cri
Ma'aikatar tsaron kasar Niger ta ba da labari a jiya Alhamis cewa, sojojin kasar da na Faransa sun harbe 'yan ta'adda 18, a wani matakin soji na hadin gwiwa da suka yi a kwanan baya a jihar Tillabéri dake yammacin kasar.

A cikin wata sanarwar da ministan tsaron kasar Niger Kalla Moutari ya gabatar a wannan rana, ya nuna cewa, sojojin bangarorin biyu sun harbi wadannan 'yan ta'adda 18 ne a wani matakin soji da suka dauka cikin hadin gwiwa daga ranar 8 zuwa 18 ga wata, a yankin Tongo-Tongo na jihar, inda kuma suka tsare wasu 'yan ta'adda 5 da kwato makamai masu dimbin yawa. Sanarwar ta ce babu wani sojan bangarorin biyu da ya rasa ransa ko ji rauni a aikin na wannan karon.

Yankin Tongo-Tongo na yammacin kasar Niger, na makwabtaka da kasar Mali a bangaren kudu maso gabas. Kuma kungiyoyi masu tsattsauran ra'ayi sun rika kai hare-hare a yammacin Niger, wuraren dake iyakokin Mali da Burkina Faso, lamarin da ya haddasa dimbin asara. (Amina Xu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China