![]() |
|
2019-06-11 11:10:29 cri |
Jakada Wu Peng ya bayyana cewa, bayan da kasar Kenya ta samu 'yancin kai, Sin ta taimaka mata da ayyuka kimanin 100 ta hanyoyin gudummawar kyauta, da rancen kudi ba tare da ruwa ba, da rancen kudi mai rangwame da sauransu, hakan ya sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al'umma da zaman rayuwar jama'ar kasar. A matsayin daya daga cikin manyan abokan kasar Kenya, Sin za ta maida hankali ga manyan ajenda hudu na kasar musamman sha'anin kera kayayyaki yayin da take samar da gudummawa ga kasar Kenya. Kana kasashen biyu sun fara horar da malamai dake da kwarewar sana'a don inganta karfin bada ilmin sana'o'i da samar da ayyukan yi da kara kudin shiga a yankin. (Zainab)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China