Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasar Sin ta nada jamian da za su sa ido wajen kare yara
2019-05-28 10:21:26        cri

Kasar Sin ta nada jami'an sa ido da masu kula da yara, a wani yunkuri na karfafa kare yara da kara kyautata bada hidima ga masu bukata.

Yayin wani taron manema labarai a jiya, Ni Chunxia, jami'i a ma'aikatar kula da harkokin al'umma ya ce kawo yanzu, an nada jami'an sa sanya ido 45,000 da masu kula da yara 620,000 a matakan garuruwa da kauyuka.

A cewar takardar ka'idoji da ma'aikatar ta fitar da hadin gwiwa sauran sassan gwamnati, aikin masu sanya idon shi ne, ziyartar yaran da iyayensu suka kaura zuwa birni suka barsu da yaran dake cikin matsanancin yanayi a akai kai, inda za su rika tattara rahoto da bayanan yaran dake bukatar taimako domin taimka musu samun tallafi.

Takardar ta kara da cewa, za kuma a horar da jami'an domin taimaka musu sauke nauyin da ya rataya a wuyansu yadda ya kamata. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China