Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-09-10 17:04:36    
Kasar Sin ta kara taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa nan da shekaru 60 da suka gabata

cri

A yayin da yake zantawa kan nasarorin da Sin ta samu a fannin gudanar da harkokin diflomasiyya tare da bangarori daban-daban, Mista Yang ya ce, tun kafuwar sabuwar kasar Sin, musamman ma tun da aka soma aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje nan da shekaru 30 da suka shige, kasar Sin na kara taka muhimmiyar rawa a fannoni daban-daban, ciki kuwa har da yin shiga-tsakani a manyan batutuwan shiyya-shiyya da na kasa da kasa, da kiyaye zaman lafiya a duniya da saurans. Yang ya furta cewa: "Kasar Sin na dukufa ka'in da na'in kan bin ka'idojin kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya, da yin kokarin shawo kan rikicin duniya ta hanyar yin shawarwari da tattaunawa."

1 2 3