Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-09-10 16:50:52    
Bikin tunawa da kafuwar jamhuriyar Libya

cri

Cikin wadannan shekaru 40 da shugaba Gaddafi yake kan karagar mulki, bai samu matsayi mai kyau ba a idanun kasashen yamma, amma nasarorin da ya samu yayin da yake kula da harkokin gida sun sa ya samu kwarjini da martaba cikin zukatan jama'ar kasar Libya, in ji Sun Lizhou, wani masanin kasar Sin da ke binciken huldar kasa da kasa.

Bayan da aka tumbuke mulkin sarakuna, an kafa jamhuriya a kasar Libya, inda aka rungumi tsarin siyasa na zamani. Sa'an nan wajen tattalin arziki, zaman rayuwar jama'ar kasar Libya ya gyaru sosai. Ban da wannan kuma, gwamnatin kasar Libya na kokarin daukaka matsayinta a duniya, bisa dimbin albarkatun kasa da Allah ya huwace wa kasar, da kuma daukan nagartattun matakan diplomasiyya.

1 2 3