Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-06-30 17:31:06    
Taron koli na kungiyar AU zai sanya muhimmanci kan ayyukan gona da kuma tsaron kai

cri

Shugabannin kasashe membobin kungiyar tarayyar Afirka wato AU za su taru a birnin Sirte na kasar Libya da ke bakin teku daga ran 1 zuwa ran 3 ga wata mai zuwa domin halartar taron koli a karo na 13 na kungiyar AU, wanda za a mayar da "sa kaimi ga karuwar tattalin arziki ta hanyar zuba jari a kan ayyukan gona da kuma tsaron shiyya-shiyya" a matsayin babban takensa.

A cikin rahoton tattalin arzikin Afirka na shekara-shekara da kwamitin tattalin arzikin Afirka na MDD da kuma kungiyar AU suka bayar, an kiyasta cewa, a shekarar da ake ciki, jimillar karuwar tattalin arzikin Afirka za ta ragu daga kashi 5.1 cikin kashi dari na shekara ta 2008 zuwa kashi 2 cikin kashi dari, amma ayyukan gona za su samar da kyakkyawar dama ga Afirka wajen fama da talauci. Haka kuma rahoton ya yi kira ga kasashen Afirka da su kara sanya muhimmanci kan ayyukan gona da kuma kara zuba jari a wannan fanni. Mayar da batun zuba jari a kan ayyukan gona a matsayin babban taken taron ya nuna muhimmin matsayin ayyukan gona a fannin sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin Afirka da kuma cimma burin samun bunkasuwa da MDD ta tsara a shekara ta 2000.

1 2 3