Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-03-19 10:46:09    
Firayiministocin kasashen Sin da Korea ta Arewa sun halarci bikin bude ' Shekarar sada zumunta tsakanin Sin da Korea ta Arewa'

cri

An labarta cewa, a duk tsawon lokacin da ake gudanar bikin shekarar sada zumunta tsakanin Sin da Korea ta Arewa, bangarorin biyu za su gudanar da harkoki iri dabam-daban kimanin 60 a fannonin siyasa, da tattalin arziki, da al'adu, da wasannin motsa jiki, da kimiyya da fasaha da kuma na tarbiyya da dai sauransu. Ban da wannan kuma, za a gudanar da harkoki iri dabam-daban na musanye-musanye da sada zumunci a kowane wata. A yi gadon abubuwan gargajiya da inganta zumunci, da habaka musanye-musanye da hadin gwiwa da kuma ci gaba cikin kafada da kafada da kirkiro kyakkyawan makoma, manyan muradai uku ne na gududanar da shagalin shekarar sada zumunta. Firaminista Wen Jiabo ya bada karin bayani kan lamarin, inda ya furta cewa : ' Gudanar da bikin shekarar sada zumunta daidai a albarkacin cikon shekaru 60 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashen Sin da Korea ta Arewa na da muhmmmancin gaske. Na yi imanin cewa, bisa kokarin da bangarorin biyu suke yi, za a iya cimma kyakkyawan burin gudanar da irin wannan biki kamar yadda aka zata a da'. ( Sani Wang )


1 2 3