Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-10-03 17:44:48    
Musulmin kasar Sin a watan azumi

cri

Da misalin karfe 9 ne, musulmi suka fara jam'i a karkashin jagorancin limamai. Bayan da aka kammala jam'i, masallacin ya shirya 'ya'yan itatuwa da sauran abinci, ya rarraba wa kowa. Sa'an nan, kowa ya koma gida. A nan kasar Sin, bayan da aka tashi daga masallaci, a kan kai wa juna ziyara, domin mika gaishe-gaishe na murnar sallah, a ci abinci tare, sa'an nan, a kan kuma je kaburburan iyalan wadanda suka rasu, domin tunawa da su.

Karamar sallah muhimmin biki ne ga musulmin duniya, musulmin kasar Sin su ma sun mika gaishe-gaishensu ga musulmi na kasashe daban daban. Da farko dai, bari malam Wang Chong'en, liman da ke masallacin Fayuan ya mika gaishe-gaishensa.

"Yau bikin karamar sallah ne ga musulmin duniya, sabo da haka, ina taya musulmin duniya baki daya murnar sallah."

Sauran musulmin kasar Sin ma suna son mika gaishe-gaishensu.


1 2 3