Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-05-05 14:38:26    
Mr. Sarkozy ya sami sakamako da yawa daga ziyararsa a Tunisia

cri
 

Amma kasashen da ke gabar kudancin tekun Bahar Rum suna fatan za a inganta dangantakar tattalin arziki da ciniki tare da kungiyar EU ta hanyar kafa wannan kawance, a maimakon koma baya, wato bin umurnin kungiyar EU.

Inganta dangantaka a tsakanin kasarsa da Tunisia, muhimmin abu ne daban da Mr. Sarkozy ya mai da hankali a kai a wannan karo. Faransa ta taba yin mulkin mallaka a Tunisia. Yanzu Faransa ta fi zuba jari a Tunisia, haka kuma, ta zama abokiya mafi girma ga Tunisia a harkokin ciniki. Yawan kudaden da suka samu daga wajen yin ciniki a shekarar 2007 ya kai kudin Euro misalin biliyan 7. Yanzu kamfanoni da masana'antu kusan 1200 na Faransa sun kafa rassansu a Tunisia, kuma sun gudanar da shirye-shirye fiye da 1400 a Tunisia.

A wannan karo, Mr. Sarkozy ya kai wa Tunisia ziyara tare da 'yan masana'antu fiye da 500, sun yi tuntuba da shawarwari tare da rukunoni daban daban na Tunisia. A gun shawarwarin, shugabannin kasashen 2 sun bayyana cewa, suna son kafa dangantakar abokantaka domin moriyar juna a tsakaninsu bisa manyan tsare-tsare.


1 2 3