Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-03-13 20:15:00    
Ma'aikatan Darfur da ke gandun noma na kasar Sin da ke birnin Khartoum

cri

A karkarar birnin Khartoum, hedkwatar kasar Sudan, da akwai wani gandun noma wanda Sinawa suka bude, ma'aikatan kasar Sudan da aka yi hayarsu cikin gandun dukkansu sun zo ne daga shiyyar Darfur. Sun ciyar da iyalansu ta hanyar aiki, sa'an nan kuma sun ba da taimako ga bunkasuwar wannan gandun noma. To jama'a masu sauraro, yanzu za mu karanta muku wani bayanin da wakilanmu suka ruwaito mana daga birnin Khartoum.

Bayan da aka shiga cikin gandun noma, kamar a shiga cikin wani karamin kauye na kasar Sin, ga kuke-kuken karnuka da na tsuntsaye, ga kuma itatuwa ko'ina, kuma ana iya ganin ganyayen lambu masu tsanwa shur suna girma da kyau cikin gonaki. Mai gandun noma Mr. Fan Chuanzhao shi ne ya karbe wakilanmu, ya ce,

"Fadin gangun noma ya kai misalin kadada 10, musamman domin shuka kayan lambu na kasa Sin, nau'orinsu kuma har da lafsur da ganye mai ba da mai da kabeji da alayyaho."


1 2 3