![]( /mmsource/images/2008/03/12/yang5.jpg)
Bayan da ministan harkokin waje na kasar Sin Mr Yang Jiechi ya takaita tarihi, sa'an nan kuma ya yi hangen nesa a kan nan gaba. A ganin minista Yang, a cikin shekaru 5 masu zuwa, a fannin diplomasiyya, kasar Sin za ta fuskanci kyakkyawar dama yayin da take fuskantar kalubale da yawa, wadda ta fi kalubale yawa. Ya ce,
'A matsayina na ministan harkokin waje na kasar Sin, ina ganin cewa, a cikin shekaru 5 masu zuwa, halin da ke tsakanin kasa da kasa zai samu yamutsi, akwai dama, kuma akwai kalubale. Sabo da haka ne, za mu mayar da kalubale da zai zama dama, za mu mayar da dama da za ta zama abin hakika, domin taimakawa kasar Sin da ta kafa wata al'umma mai jituwa a fannoni daban daban, da kuma samar da wata kyakkywar makoma tare da jama'ar kasa da kasa. Ina da imani sosai game da makomar kasar Sin da ta duk duniya.'(Danladi) 1 2 3
|