Lokacin da yake zantawa da manema labaru, magajin birnin Shanghai malam Han Zheng ya ce,'Za mu mayar da shirya taron wasannin Olympic na musamman na wannan karo yadda ya kamata tamkar wata sabuwar dama, wato za mu kara bunkasa sha'anin wasannin Olympic na musamman da na nakasassu na Shanghai daga dukkan fannoni.'
Kasashen duniya sun kara mai da hankulansu kan kasar Sin da kuma Shanghai domin taron wasannin Olympic na musamman, sa'an nan kuma, nakasassu a kwakwalwa sun ji dadin zamansu a Shanghai mai wadata. Mutane na nuna wa wadannan mutane da suka sha bamban da saura irin kauna ta musamman, a sa'i daya kuma, ana mayar da mutane a gaban kome a Shanghai, har ma a duk kasar Sin.(Tasallah) 1 2 3
|