Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-10-01 18:00:04    
Za a sake yin shawarwari tsakanin shugabannin kasashen Korea ta kudu da ta arewa

cri
 

Bayan shekaru 7 da aka yi ana shawarwari a karo na farko tsakanin shugabannin kasashen Korea ta kudu da ta arewa, ga shi kuma banganrorin 2 sun sake yin shawarwari tsakanin shugabanninsu. A ran 5 ga watan Agusta na wannna shekara, Korea ta kudu da ta arewa sun bayar da "Yarjejeniyar tsakanin kudu da arewa" a sa'i daya dangane da shawarwarin da za a yi a birnin Pyongyang a tsakanin shugaba Roh Moo Hyun na Korea ta kudu da shugaba Kim Jong Il na Korea ta arewa. Yarjejeniyar ta bayyana cewa, bisa harsashen tattara sakamakon da bangarorin 2 suka samu cikin shekaru 7 da suka wuce wajen samun sulhuntawar al'umma da yin hadin gwiwa tsakaninsu, za su tattauna matsalolin kara amincewa juna da kafa tsarin shimfida zaman lafiya a zirin Korea, da kuma kyautata hadin gwiwa a tsakaninsu wajen tattalin arziki.

Bayan da Korea ta kudu da ta arewa suka yi shalar yin shawarwarin karo na 2 a tsakanin shugabanninsu, bangarorin 2 kuma sun yi shawarwari sau da dama a tsakaninsu, har sun samu ra'ayi daya kan jadawalin shawarwarin shugabanninsu da yawan mutanen kungiyar wakilan kasar Korea ta kudu, da hanyar da kungiyar za ta bi wajen yin ziyara.


1 2 3