Abin da muke so mu gaya muku shi ne, gwamnatin kasar Sin ta fi mayar da hankalinta kan bunkasa kyakkyawar dangantakar hadin gwiwa tare da sauran kasashe da jihohi da kuma kungiyoyin da abin ya shafa na kasa da kasa a fannin ayyukan samar da ingantaccen abinci. Malam Luo Yunbo ya furta cewa : ' Kara yin hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa a fannin samar da ingantaccen abinci, ba ma kawai zai bada amfani ga tsara ma'auni iri daya na dudduba ingancin abinci ba, har ma zai ingiza bunkasuwar cinikayyar da ake yi tsakanin kasa da kasa.'
A karshe dai, takardar bayanin ta nuna cewa, kasar Sin kasa ce mai tasowa. Don haka, ya kasance da gibi tsakaninta da kasashe masu sukuni a fannin sarrafe-sarrafen abinci a matsayin masana'antu. Kasar Sin tana so ta sanya kokari tare da sauran kasashen duniya wajen bunkasa cinikin abinci tsakanin kasashen duk duniya lami-lafiya. ( Sani Wang ) 1 2 3
|