Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-08-01 16:53:47    
Kungiyar 'yantar da Palasdinu

cri

Da ma a farkon kafuwarta, burin kungiyar PLO shi ne murkushe akidar siyasa ta Yahudawa daga fannonin siyasa da tattalin arziki da soja da al'adu ta hanyar nuna karfin soja, sa'an nan, a kafa kasar Palasdinu a yankin Palasdinu. Kungiyar ta taba fafatawa a kasashen Jordan da Lebanon a matsayin sansanoninta. Bayan da Isra'ila ta kutsa kai cikin Lebanon a shekarar 1982, PLO ta sha asarori a fannin soja, ba yadda ta yi sai ta janye jikinta daga birnin Beirut.

Sakamakon sauye-sauyen halin da ake ciki a gabas ta tsakiya, kungiyar PLO ta fara daukar sassaucin matsayi kan batun Palasdinu. A ranar 15 ga watan Nuwamba na shekarar 1988, an zartas da sanarwar siyasa da sanarwar samun 'yancin kai a gun taron musamman na majalisar kasa ta kungiyar, inda aka sanar da amincewa da kuduri mai lambar 242 da 338 na MDD, aka kuma sanar da kafuwar kasar Palasdinu.(Lubabatu)


1 2 3