Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-06-05 15:22:22    
An soma tuhuma kan laifufukan da tsohon shugaban kasar Liberiya Charles Taylor ya yi a birnin Hague na kasar Netherland

cri

A watan Janairu na shekarar da ta gabata, wata shugaba mai ci Ellen Johnson Sirleaf ta kasar Liberia ta yi rantsuwar hau kujerar mulkin kasar, a farkon watan Maris na wannan shekara, sabuwar gwamnatin kasar Liberia ta gabatar da bukatarta na mayar da Taylor, bayan da kasar Nijeriya ta amince da bukatar, sai Taylor ya gudu a daren ranar 27 ga watan Maris na shekarar da ta gabata, a daren ranar 28 ga watan Maris na wannan shekara, rundunar sojojin tsaron kai ta kasar Nigeriya ta kama shi a wurin da ke tsakanin iyakar kasar Nijeriya da Kamaru, kuma an kai shi zuwa hedkwatgar kasar Liberia, sa'anan kuma gwamnatin Liberia ta mika shi ga Kotun Musamman ta Majalisar Dinkin Duniya ta kasar Saliyo.don kawar da rikicin da zai faru a kasar Saliyo, an kai Tailor zuwa birnin Hague don yi masa tuhuma. Sa'anan kuma, kwamitin sulhu na Majalisar dinkin duniya ya zartas da kuduri na yi wa Taylor tuhuma a kotun musamman da ke birnin Hague.

Kafin wannan, Taylor ya musunta dukkan karar da aka yi masa, za a bin bahasin laifufukan Taylor a cikin watanni 18, kuma yawan masu ba da shaida zai kai 140. Idan an tabbatar da laifufukan da ya yi, to za a tsare shi cikin gidan aya har dukkan rayuwarsa a duniya.(Halima)


1 2 3