Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-10-17 17:36:20    
Kasar Sin da kasar Masar su ne abokai masu kirki kuma aminai da 'yanuwa masu kirki a tsakaninsu

cri

Jakada Wu Sike ya ci gaba da cewa, kasashen biyu dukansu suna mai da hankali ga raya al'adu, a sa'I daya kuma, dukansu suna tsayawa tsayin daka don yin shawarwari a tsakaninsu bisa bambancin wayin kai da kuma yin ma'amala a tsakaninsu, ba su amince da ra'ayin yin hargitsi bisa bambancin wayin kai da ke kasancewa a tsakaninsu. Saboda haka har wa yau dai kasashen biyu suke yin ma'amala a tsakaninsu cikin himma da kwazo.

Jakada Wu Sike ya gaya wa manema labaru cewa, shugaban kasar Masar Mubarak zai halarci taron koli na yin dandalin tattaunawa kan hadin guiwa a tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika wanda za a kira a nan gaba ba da dadewa ba.Ya kuma bayyana cewa, shugaba Mubarak zai kai ziyarar aiki a kasar Sin.(Halima)


1  2  3