Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-07-28 20:30:54    
An yi bukukuwa a birnin Tangshan na kasar Sin don tunawa da cikon shekaru 30 da aka yi girgizar kasa a wurin

cri

Yau Jumma'a ranar 28 ga wata, rana ce ta cikon shekaru 30 da aka yi girgizar kasa a birnin Tangshan na kasar Sin, a ran nan, an yi jerin bukukuwa a birnin Tangshan don tunawa da yaki da girgizar. A gun taron da aka yi a wannan rana don tunawa da cikon shekaru 30 da aka yaki da girgizar kasa, sakataren kwamitin jam'iyyar kwaminis ta birnin Tangshan, Mr.Zhang He ya ce, a cikin shekaru 30 da suka wuce, birnin Tangshan ya sami manyan sauye-sauye a fannonin manyan ayyuka da ilmi da al'adu da kiwon lafiya da dai sauransu, kuma an yi ta kyautata zaman rayuwar mazaunan birnin sama da miliyan 7.

A ran 28 ga watan Yuli na shekara ta 1976, an yi girgizar kasa da karfinta ya kai digiri 7.8 bisa ma'aunin Richter a birnin Tangshan na lardin Hebei da ke arewacin kasar Sin. sakamakon girgizar, mutane fiye da dubu 240 sun mutu, a yayin da wasu sama da dubu 160 sun ji raunuka, kuma birnin Tangshan ya zama kufayi.


1  2  3