Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-04-17 17:53:07    
Zantutukan da aka yi kan nasara da hasara da aka samu bisa sakamakon samun makaurata na kasashen Afrika

cri

Kasashe masu ci gaba su ma suna kasancewa da halinsu na fannoni biyu, a wani fanni, suna fatan kasashe masu wadata  za su dauki manufofin nuna sassauci kan  makaurata, ta haka, za su iya kara samun kudadden musaya, a sa'I daya kuma za su iya koyo da kuma shigar da fasahohin kimiyya na zamani daga kasashe masu wadata, A wani fanni daban, a wajen sassan da suka yi karancin kwararru, kasashe masu tasowa su ma sun kai suka ga kasashe masu ci gaba saboda sun kwace kwararrunsu, wannan ya kara tsananta rikicin da suke gamuwa da shi.

A watan jiya, Makauratan kasar Kenya sun kafa wata kungiya, wadda ta tsai da kuduri cewa, za ta zuba jari da yawansu zai kai kudin Amurka dolla miliyan dari ga kasar Kenya a cikin shekaru biyar masu zuwa don raya tattalin arzikin kasar. Kafofin watsa labaru na kasar sun nuna yabo sosai ga wannan.

Kasashen Afrika sun yi farin ciki tare da damuwa. Manazartan al'amura na yau da kullum sun bayyana cewa, makauratan da ke zama a kasashen waje sun kawo moriyoyi da yawa ga kasashen Afrika, amma batun makaurata shi ma ya kawo babban kalubale ga wadannan kasashe wajen kiwon lafiya da sauran fannoni, saboda haka ya kamata kasashen Afrika su nemi hanyar da za su bi don daidaita batun.


1  2  3